Kamfanin dillancin labaran kasa da kasa na Ahlul Baiti (AS) – ABNA - ya habarta cewa: tashar talabijin ta kasar Iran ta bayar da rahoton cewa, an kashe fararen hula 60 a harin da yahudawan sahyuniya suka kai a daren jiya.
Tashar talabijin ta Iran ta bayar da rahoton cewa, dukkan wadanda aka kashen fararen hula ne da suka hada da kananan yara 20, tare da yin nuni da cewa, dakarun yahudawan sahyoniya sun kai hari a wani yanki da ke yankin Jamaran da ke gabashin babban birnin kasar Iran.
Tashar talabijin ta Iran ta kara da cewa har yanzu ana ci gaba da kwashe gawarwakin shahidan, kuma ana sa ran adadin zai karu. A jiya manyan yankuna na Jamhuriyar Musulunci ta Iran sun fuskanci mummunar wuce gona da iri daga bangaren sahyoniyawan mamaya.
Your Comment